Tushen wani gini ya rushe a wajen haƙarasa da ke cikin Radio House a Abuja, lamarin da ya yi sanadin mutuwar wani matashi mai shekaru 25.
Hukumar Kwantar da Wuta ta Ƙasa (FFS) ta tabbatar da faruwar lamarin, inda ta ce jami’anta sun amsa kiran gaggawa a ranar Lahadi, 24 ga watan Agusta, 2025.
Jami’in hulɗa da jama’a na FFS a matakin ƙasa, DCF P.O. Abraham, ya bayyana cewa tawagar ceto ta fito da gawar mamacin daga cikin rusasshen wajen sannan aka mika ta ga iyalansa.
Hukumar ta bayyana ta’aziyyarta ga dangin mamacin tare da yin kira ga kamfanonin gine-gine da su riƙa bin ƙa’idojin tsaro domin kauce wa irin wannan mummunan lamari a nan gaba.
“Hukumar Kwantar da Wuta ta Ƙasa tana jajanta wa dangin da abin ya shafa tare da yin kira ga kamfanonin gine-gine da su tabbatar da bin ƙa’idodin tsaro domin kauce wa sake faruwar irin wannan al’amari,” in ji sanarwar.
Wannan na zuwa ne a matsayin sabon lamari a jerin rushewar gine-gine da ke ta faruwa a Babban Birnin Tarayya (FCT). A watan Yuli 2025, wani ginin bene mai hawa biyu da ake ginawa a Gwarinpa ya rushe, inda mutane biyu suka mutu.
Haka kuma a watan Mayu 2025, wani gini da bai kammalu ba a unguwar Jabi ya kife sakamakon ruwan sama, inda ma’aikatan gine-ginen suka makale a ciki. A watan Maris 2025 kuma, mutane akalla uku ne suka rasa rayukansu a wani rushewar gini a Kubwa.
Masana harkar ci gaban birane da kungiyoyin farar hula sun sha nuna damuwa kan irin wannan bala’i, inda suka dora alhakin hakan kan rashin ingantaccen aikin injiniya, amfani da kayan gini marasa kyau, da kuma kin bin tsare-tsaren gine-gine.
Maƙwabta da al’umma sun bukaci Hukumar Ci gaban Babban Birnin Tarayya (FCDA) da sauran hukumomin da abin ya shafa da su ƙara tsaurara sa ido kan ayyukan gine-gine tare da hukunta masu yin karya ƙa’ida.



