Ministan Ayyuka, David Umahi, ya bayyana cewa aikin gyaran tsarin gadon Gada ta Third Mainland da ke jihar Legas zai kashe kusan Naira tiriliyan 3.6, yana gargadin cewa lalacewar tsarin gada a karkashin ruwa na barazana ga gadar da tafi kowacce cunkoso a kasar.
Yayin da yake zantawa da manema labarai bayan taron Majalisar Zartarwa ta Tarayya (FEC) a ranar Laraba a Abuja, Umahi ya ce binciken da aka yi kwanan nan ya gano lalacewa mai tsanani a kan ginshikai da turakun gadar, wanda hakan ya samo asali ne daga haramtaccen tono yashi, hura kasa, da kuma lalacewar ƙarfe.
Ya kara da cewa, an kiyasta kudin aikin gyaran ya kai Naira tiriliyan 3.8, yayin da gina sabuwar gada daga farko zai kashe kadan kasa da hakan, wato Naira tiriliyan 3.6.
“Muna da amincewa don aƙalla kwararru kamfanoni bakwai su gudanar da cikakken bincike, zane-zane, da kuma bada kwangila ga aikin gyara da gina sabuwar gada a karkashin tsarin EPC+F [Injiniya, Siyan Kayan Aiki, Gina da Samar da Kudi],” in ji ministan.
Ya ce wannan bincike ya yi kama da wanda aka yi a kan Gada ta Carter, wadda ke Legas, inda kamfanin Julius Berger ya ce ba ta da amfani wajen gyara kuma ya bada shawarar gina sabuwa, da aka kiyasta kudinta zai kai Naira biliyan 359.
A karkashin amincewar FEC, gwamnati za ta sanar da bude damar yin gasa a karkashin tsarin hadin gwiwar gwamnati da masu zaman kansu (PPP) don gudanar da aikin, tare da tattaunawa da masu bayar da lamuni na kasa da kasa, ciki har da Deutsche Bank.
“Lalacewar karkashin ruwa ta samo asali ne daga shekaru na sakaci da ayyukan bil’adama da suka raunana tushen gadar,” in ji shi.
“Ba za mu iya bata lokaci ba. Ko dai mu gyara ko mu gina sabuwa, kudade da ƙwarewar injiniya da ake bukata suna da yawa matuka.”
Umahi ya kuma bayyana amincewar FEC wajen yin gaggawar gyaran wasu gadar da suka lalace a fadin kasar, ciki har da Gadar Jalingo a jihar Taraba, Gadar Ido (da wuta ta lalata), Flyover din Keffi a jihar Nasarawa, Gadar Mokwa a jihar Neja, wata gada a kan hanyar Abuja–Kogi, wasu gada a kan hanyar Legas–Ibadan da motoci suka bugo, Gadar Jebba a jihar Kwara, da kuma Gadar Itokin–Ikorodu a Legas.
“Za a rubuta duk wadannan aikin gaggawa a tura su ga shugaban kasa domin amincewa ta hanyar ma’aikatar kudi,” in ji shi.
An kaddamar da Gada ta Third Mainland a shekarar 1990, wadda ita ce mafi tsawo a Najeriya, kuma tana da matukar muhimmanci wajen sufuri ga mutanen Legas da ake kiyasta sun kai miliyan 20.
An taba yi mata gyare-gyare lokaci zuwa lokaci, amma Umahi ya ce binciken baya-bayan nan ya gano lalacewar ginshikan karkashin ruwa fiye da yadda aka taba sani a baya.



