Lauyan kare hakkin dan Adam kuma Babban Lauya a Najeriya (SAN), Femi Falana, a ranar Lahadi ya caccaki hukumar National Youth Service Corps (NYSC) kan matakin da ta dauka na rike takardar kammala aikin yi wa kasa (discharge certificate) ta Ushie Uguamaye, wadda aka fi sani da Raye, a bisa zargin ramuwar gayya saboda suka da ta yi wa manufofin tattalin arziki na gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.
Falana, a cikin wata sanarwa, ya bayyana wannan mataki a matsayin nuna son kai da gaggawa ba tare da bin ka’ida ba. Ya ce rike takardar ba bisa doka ba ne domin babu wani kotu mai hurumin da ta ba da umarnin hakan.
“Lamarin yana tuna mana da abin da ya faru a shekarar 1988 lokacin da hukumar NYSC ta kwace takardar kammala aikin yi wa kasa ta marigayi Bamidele Aturu, saboda ya ki karbar kyautar Best Corper Award bisa dalilin cewa bai son ya yi musafaha da Gwamnan Sojan Jihar Neja, Lt. Col. Lawan Gwadabe. Wannan ya faru ne a zamanin mulkin soja na Ibrahim Babangida lokacin da an takaita ‘yancin dan Adam,” in ji Falana.
Ya kara da cewa, tun da Najeriya tana karkashin mulkin dimokiradiyya, Rita Uguamaye tana da ‘yancin yin suka ga gwamnati kamar yadda Sashe na 39 na Kundin Tsarin Mulkin Tarayyar Najeriya na 1999 ya tanada.
Falana ya tunatar da hukumar NYSC jawabin Shugaba Tinubu a ranar Democracy Day, inda ya gargadi jami’an gwamnati kada su danne ra’ayoyin jama’a, domin hakan na iya haifar da tashin hankali da kuma raunana dimokiradiyya.
“Shugaban kasa ya bayyana cewa, ‘Duk da cewa batanci da karya bai kamata a yi watsi da su ba, babu wanda ya kamata a zalunce shi saboda kawai ya rubuta rahoton da bai yi min dadi ba ko ya yi min kira.’ A bisa wannan alkawarin Shugaba na karfafa wa ‘yan Najeriya gwiwar yin suka ga gwamnati, hukumar NYSC ta gaggauta sakin takardar kammala aikin yi wa kasa ta Rita Uguamaye ba tare da wani jinkiri ba,” in ji Falana.
Raye ta shahara a kafafen sada zumunta ne bayan ta soki gwamnatin Tinubu, tana bayyana cewa manufofinta sun kara tsananta halin tattalin arzikin kasar.
A cikin wani faifan bidiyo da ta wallafa a shafinta na TikTok @talktoraye, Uguamaye ta nuna bacin rai kan tsadar rayuwa, hauhawar farashin kaya da kuma halin kunci, tare da zargin Shugaban kasa a matsayin “mummunan shugaba” da rashin iya magance matsalolin tattalin arziki da jama’a ke fuskanta.
