Shugaban kungiyar IPOB mai goyon bayan kirkirar Biafra, Nnamdi Kanu, wanda ake tsare da shi, ya janye daga shirin da ya ke da niyyar kiran shaidu don kare kansa a shari’ar da ake masa kan zarginsa da aikata laifukan ta’addanci.
Kotun ta dage zaman shari’ar zuwa ranar 27 ga watan Oktoba domin Kanu ya bayyana kare kansa. Shugaban IPOB ya rubuta wa kotun yana bayyana niyyar kiran shaidu tare da neman izinin kiran su, sannan ya roki kotun ta ba shi lokaci ya duba takardun shari’ar.
Lokacin da aka fara shari’ar ranar Litinin, Kanu ya ce ya duba takardun shari’ar kuma ya fahimci cewa babu wani hujja mai inganci a kansa.
Ya bayyana cewa tun da yake ya tabbatar da cewa babu wani zargi mai inganci a kansa kuma cewa an yi masa shari’a ba bisa ka’ida ba, ba zai yi bukatar yin kariya ba.
Mai shari’a James Omotosho ya umurci Kanu ya rubuta wasika bisa ga wannan ra’ayi sannan ya mika wa masu gabatar da kara.
Mai shari’ar ya shawarci Kanu ya tuntuɓi ƙwararru a fannin doka don fahimtar sakamakon wannan zabin da ya zaba.
Bayan haka, mai shari’a ya dage zaman zuwa ranar 4, 5, da 6 ga Nuwamba domin karɓar ƙarshe na rubutattun jawaban bisa matsayin wanda ake tuhuma cewa shaidun da aka gabatar har yanzu ba su kafa wani zargi a kansa, ko kuma wanda ake tuhuma zai shigar da kare kansa.

