Trends

Sabbin Haraji: Najeriya Ta Shiga Sahun Kasashen Da Trump Ya Kakabawa

Shugaban Kasar Amurka, Donald Trump, ya sanya sabbin haraji na kashi 15% kan kaya daga Najeriya da wasu kasashen Afirka.

A cewar sanarwar da Fadar White House ta fitar a ranar Alhamis, wannan sabon umarnin mai taken “Further Modifying the Reciprocal Tariff Rates” (Ci gaba da Sauya Kudaden Harajin Sauyawa) zai fara aiki daga karfe 12:01 na safe ga duk wani kaya da aka shigo da shi domin amfani a cikin kasar Amurka ko kuma da aka cire daga rumbun ajiya domin amfani.

Kasashen da wannan haraji ya shafa sun hada da: Najeriya, Zimbabwe, Zambia, Uganda, Mozambique, Mauritius, Ghana, Malawi, Lesotho, da Madagascar.

A cewar umarnin shugaban, an kakaba haraji daban-daban kan wasu kasashe kamar haka:

Kashi 30% – Afirka ta Kudu da Libya

Kashi 25% – Tunisia

Kashi 10% – Falkland Islands, Birtaniya, da sauran kasashen da ba a lissafa ba

Kashi 15% – Najeriya da wasu kasashe da suka hada da Ghana, Uganda, Japan, Iceland, New Zealand, da dai sauransu

Kashi 20% – Bangladesh, Thailand, Taiwan, Vietnam da Sri Lanka

Kashi 25% – Indiya, Tunisia, Brunei da Kazakhstan

Kashi 30% – Algeria da Bosnia

Kashi 35% – Iraq da Serbia

Kashi 40% – Laos da Myanmar (Burma)

Kashi 41% – Syria

Tun a watan Afrilu, Trump ya kakabawa Najeriya haraji na kashi 14% a matsayin wani bangare na tsarin harajin sauyawa na kasuwanci tsakanin kasashen duniya. Sai dai daga bisani aka dakatar da aiwatar da harajin na tsawon kwanaki 90 domin bada damar tattaunawa da kasashe a kan yarjejeniyoyin kasuwanci na musamman.

Wa’adin tattaunawar ya kare ne a ranar 1 ga watan Agusta, inda daga wannan rana aka fara aiwatar da sabbin matakan haraji.

Wannan mataki yana da tasiri ga kasashen da ke cinikayya da Amurka, musamman kasashen da suka dogara da fitar da kayayyaki zuwa kasuwar Amurka. Najeriya na daya daga cikin kasashen da hakan zai shafa, musamman bangaren masana’antu da fitar da kayayyaki irin su man gyada, kayayyakin noma, da kuma wasu kayayyakin sarrafa gida.