Trends

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar da Asibitin Kwararru Mai Gado 100 a Kaduna

Bola Ahmed Tinubu Shugaban Kasar Nigeriya

Gwamnatin Tarayya ta kaddamar da wani sabon asibitin kwararru mai gadaje 100 mai suna “Renewed Hope Specialist Hospital” a birnin Zaria na jihar Kaduna State, a wani bangare na kokarin fadada samun ingantaccen kiwon lafiya da kuma cimma burin ci gaba mai dorewa na uku (SDG 3) wanda ya shafi lafiya da walwala.

An gudanar da aikin ne ta hannun Ofishin Babbar Mai Bai Wa Shugaban Kasa Shawara ta Musamman kan Manufofin Ci Gaba Mai Dorewa, Office of the Senior Special Assistant to the President on SDGs (OSSAP-SDGs), domin rage cunkoso a cibiyoyin lafiya da kuma samar da kulawa mai sauki ga al’ummar Kaduna da yankunan da ke makwabtaka da ita.

Babbar Mai Bai Wa Shugaban Kasa Shawara ta Musamman kan SDGs, Princess Adejoke Orelope-Adefulire, ta bayyana asibitin a matsayin wani muhimmin mataki na cike gibin da ake da shi a bangaren lafiya.

Ta ce, “Kiwon lafiya ba wata alfarma ba ce, wajibi ne. Kowace uwa na da hakkin samun kulawar haihuwa cikin aminci, sannan kowane yaro na da hakkin samun rayuwa mai kyau tun daga farko.”

Asibitin na dauke da dakunan tiyata na zamani, dakunan kula da marasa lafiya bayan tiyata, dakunan duba marasa lafiya, dakunan gwaje-gwaje, dakunan kwantar da marasa lafiya, na’urorin duban dan tayi (ultrasound), da kuma kayan agajin gaggawa domin tabbatar da cikakkiyar hidimar lafiya.

Shugaban Majalisar Wakilai ta Tarayya, Abbas Tajudeen, wanda ya taka rawa wajen samar da aikin, ya ce hakan na nuna kudirin gwamnati na mayar da manufofi zuwa ayyukan da za su amfani jama’a musamman yankunan da ba su da wadatattun kayayyakin more rayuwa.

Shi ma Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya yabawa wannan shiri, yana mai bayyana shi a matsayin “abin da ya zo a kan lokaci kuma mai matukar amfani,” tare da yin alkawarin tabbatar da amfani da asibitin yadda ya kamata da kuma dorewarsa.

Masu ruwa da tsaki da suka halarci bikin kaddamarwar sun jaddada muhimmancin kula da lafiyar mata da yara, samar da dama iri daya ga kowa wajen samun lafiya, da kuma karfafa cibiyoyin lafiya a matakin karkara.

Ana sa ran sabon asibitin zai taimaka matuka wajen inganta harkokin kiwon lafiya, rage nauyin da ke kan tsofaffin asibitoci, tare da karfafa kokarin Najeriya na gina tsarin lafiya mai dorewa da bai wa kowa dama.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *