Trends

Biyan Kuɗin Jinya Kai Tsaye na Haddasa Mutuwar da Za a Iya Kauce Wa – NMA

Kiwon lafiya Kiwon lafiya

Ƙungiyar Likitoci ta Najeriya (NMA) a Jihar Akwa Ibom ta yi gargadin cewa dogaro da biyan kuɗin jinya kai tsaye (out-of-pocket) a Najeriya na haddasa mutuwar da za a iya kauce wa, inda ta buƙaci gwamnati ta mayar da hankali kan samar da inshorar lafiya ga kowa.

Shugaban ƙungiyar a jihar, Dakta Aniekan Peter, ya ce ya kamata a bai wa bangarorin lafiya da ilimi fifiko, tare da samar da kuɗin inshorar lafiya daga harajin masana’antu ko kuma VAT.

Ya ce, “Idan aka shigar da kowa cikin tsarin, mutane za su rika zuwa asibiti idan sun kamu da rashin lafiya, domin sun san ba za su biya kuɗi ba. Hakan zai rage rikice-rikice da mutuwar da za a iya kauce wa.”

Dakta Peter ya soki yadda gwamnati ke kashe kuɗi kan shirye-shiryen tallafawa jama’a maimakon inshorar lafiya, yana mai cewa samun damar jinya kyauta zai ceci rayuka da dama.

Ya ƙara da cewa, “Mutane da yawa ba sa zuwa asibiti saboda tsadar jinya, kuma hakan na janyo mutuwar da za a iya kauce wa.”

Dangane da ƙauracewar likitoci zuwa ƙasashen waje, ya gargadi cewa ƙarancin albashi da rashin ƙarfafawa na sa likitoci barin ƙasar.

Ya ce, “Albashin likita ma ba zai iya siya masa mota ko gina masa gida ba… dole ne gwamnati ta taimaki likitoci kafin lokaci ya kure.”

Ya kuma yi magana kan yaƙi da masu aikin jinya ba bisa ka’ida ba (quackery), yana mai cewa an kafa rundunar haɗin gwiwa a Akwa Ibom, amma tana buƙatar ƙarin goyon bayan gwamnati.
Ya ce, “Idan ba a kai rahoto ba, ba za mu sani ba. Sai mun sani ne za mu je mu bincika wurin da ake zargi.”

Dakta Peter ya bayyana samun damar zuwa cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko a jihar a matsayin “mai kyau kaɗan,” amma ya jaddada buƙatar gyare-gyare, samar da gidajen ma’aikata, da ɗaukar sabbin ma’aikata.
Ya kuma buƙaci a kafa Cibiyar Kiwon Lafiya ta Tarayya (FMC) a Akwa Ibom, yana mai cewa jihar na fuskantar ƙarancin irin waɗannan cibiyoyi idan aka kwatanta da wasu jihohi.

Game da walwalar ma’aikata, ya ce an sake duba alawus-alawus na likitoci, wanda ya sa ma’aikatan lafiya a Akwa Ibom suka zama mafi yawan albashi a Najeriya.

Ya ce ana ci gaba da ɗaukar ma’aikatan lafiya 5,000, tare da gyaran asibitoci a ƙarƙashin dokar gaggawa da aka ayyana a fannin lafiya.

A ƙarshe, ya buƙaci jihar ta kafa Jami’ar Kiwon Lafiya ta Ibom, yana mai cewa wasu jihohi sun riga sun mallaki jami’o’in lafiya da dama.

“Akwa Ibom bai kamata ya zama banda ba,” in ji shi, yana mai jaddada cewa faɗaɗa ilimin kiwon lafiya na da muhimmanci wajen biyan buƙatun da za su taso a nan gaba.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *