Adelabu Ya Tabbatar da Mayar da Wutar Lantarki Cikin Kwana 14

Ministan Wutar Lantarki, Adebayo Adelabu, ya bayyana cewa gwamnati na ci gaba da kokarin shawo kan matsalolin karancin iskar gas da ke haifar da rashin isasshen wutar lantarki a Najeriya.

Da yake jawabi a wani taron manema labarai a Abuja ranar Talata, ministan ya amince da cewa jama’a na fuskantar matsin lamba sakamakon rashin wutar lantarki. Ya bayyana cewa matsalar ta samo asali ne daga karancin iskar gas, amma gwamnati na sa ran cewa matakan da ake dauka za su haifar da ingantuwar wutar lantarki a fadin kasar cikin kwanaki 14 masu zuwa.

Adelabu ya ce an riga an fara aiwatar da wasu tsare-tsare na musamman domin tabbatar da wadatar iskar gas ga tashoshin samar da wutar lantarki. Ya nuna kwarin gwiwa cewa wadannan matakai za su kawo sauyi a hankali, wanda zai amfani gidaje da kuma kasuwanci.

“Na na son in ba ‘yan Najeriya hakuri a hukumance kan wannan matsala ta wucin gadi da ke haifar da wahala, musamman a wannan lokacin na rani,” in ji Adelabu. Ya kara da cewa harkokin kasuwanci, makarantu da masana’antu sun fuskanci kalubale, amma matsalar ta samo asali ne daga wasu dalilai da ba su karkashin ikon ma’aikatar ba.
Ministan ya ce ana sa ran ganin sauyi cikin makonni biyu masu zuwa.

A halin yanzu, wani kwamiti na sa ido kan yadda kamfanonin gas ke bin dokar samar da gas ga cikin gida, domin tabbatar da cewa tashoshin wutar lantarki suna samun iskar da suke bukata. Haka kuma, gwamnati na ganin cewa fara biyan kudade ga masu samar da gas zai kara musu kwarin gwiwa wajen ci gaba da samar da shi.

Adelabu ya tabbatar wa jama’a cewa gwamnati na aiki tukuru domin inganta wutar lantarki a kasar, tare da shirin kara yawan wutar da ake samarwa zuwa megawatt 6,000 kafin karshen shekarar nan.

“Mun na aiki ba dare ba rana domin mu dawo kan turbar da muka dauka a shekarar 2025, lokacin da jama’a suka yaba da ci gaban da aka samu,” in ji shi. Ya kara da cewa burin gwamnati shi ne ta zarce matakin da aka kai a baya, musamman yayin da shekarar zabe ta 2026 ke karatowa.

Baya ga samar da wutar lantarki, Adelabu ya ce za a kuma inganta bangarorin watsa wuta da rabon ta. Ya jaddada cewa burin kaiwa megawatt 6,000 kafin karshen shekara na nan daram domin amfanin dukkan ‘yan Najeriya.