Jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ta yaba wa gwamnatin tarayya bisa “gaggawar da ta nuna wajen shawo kan yunƙurin juyin mulki a Jamhuriyar Benin,” tana mai kira ga gwamnati da ta nuna irin wannan ƙarfin hali da jajircewa wajen yaƙar ta’addanci da ’yan bindiga a cikin gida.
A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun jam’iyyar na kasa, Mallam Bolaji Abdullahi, ya fitar, ADC ta ce duk da cewa gwamnati ta nuna saurin daukar mataki a Benin, hakan “ya sake bayyana a fili yadda martanin gwamnati kan matsalolin ’yan bindiga da laifukan tarzoma a sassan Najeriya ke kasancewa mai rauni da gaj
