Trends

Shugaban FCT Ta Yaba wa Mambobi Kan Nasarar Makon ‘Yan Jarida Na Shekarar 2025

Shugaba Grace Ike da Sauran membobin ta

Shugabar kungiyar ‘yan jarida ta Najeriya, reshen Babban Birnin Tarayya (NUJ FCT), Kwamared Grace Ike, ta bayyana godiya ta musamman ga mambobin kungiyar saboda irin gagarumar gudummawar da suka bayar wajen tabbatar da nasarar bikin Makon ‘Yan Jarida na 2025.

A cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Asabar, Kwamared Ike ta yaba da hadin kai, kishin aiki, da kuma kwarewar da mambobin suka nuna a dukkanin ayyukan da aka gudanar cikin makon, inda ta ce wannan ne ya zama ginshikin nasarar wannan muhimmin biki.

“Ina mika godiya ta musamman ga dukkan mambobin NUJ FCT da suka fito kwansu da kwarkwata don halartar Makon ‘Yan Jarida na 2025. Sha’awar ku, sadaukarwa da hadin kan ku sun kasance ginshikan nasarar wannan taro,” in ji ta.

Shugabar ta kuma yi kyakkyawan yabo ga mambobin kwamitin zartarwa (EXCO) na kungiyar saboda jajircewarsu da kuma hangen nesa wajen jagorantar ayyukan, wanda hakan ya bai wa taron inganci da daukaka.

Har ila yau, Kwamared Ike ta jinjinawa Kwamitin Shirya Makon ‘Yan Jarida da Rt. Evelyn Onyilo ke jagoranta, saboda yadda suka gudanar da shirin cikin tsari da kwarewa, wanda ya tabbatar da cewa kowanne bangare na shirin ya tafi yadda ya kamata.

“Ina matukar yaba wa mambobin kwamitin zartarwa bisa jajircewarsu da kuma kwamitin shirya makon da Rt. Evelyn Onyilo ke jagoranta bisa yadda suka shirya da kuma gudanar da ayyukan cikin tsari,” ta kara da cewa.

Ta kuma nuna godiya ga tsofaffin shugabannin NUJ FCT bisa irin tallafi da shawarwarin da suke ci gaba da bayarwa, tana mai cewa ginshikan da suka kafa sun ci gaba da zame wa sabbin shugabanni madubi da jagora.

Shugabar NUJ ta kuma jinjinawa shugabannin majalisu na cibiyoyi daban-daban (chapels)—shugabanni da sakatarori—bisa yadda suka yi nasarar tunkarar mambobi a matakin kasa, abin da ya taimaka sosai wajen ganin cewa an samu gagarumar halarta da shiga cikin ayyukan.

Ba a manta da gogaggun ‘yan jarida ba, domin Kwamared Ike ta nuna godiya bisa shekarun da suka shafe suna hidima, horar da sabbin jarumai, da kuma irin gudummawar da suka bayar wajen gina kungiyar.

Ta kuma yabawa gidajen jarida da kafafen sada zumunta da suka dauki nauyin yada abubuwan da suka wakana a yayin Makon ‘Yan Jarida na 2025, tana mai cewa sun taka muhimmiyar rawa wajen yada manufofi da muradun kungiyar.

“Dukkan gudummawar da kuke bayarwa na nuna karfin hadin kai, kishin kungiya da sadaukarwa. Mu ci gaba da ginawa kan wannan ci gaba domin kare ‘yancin fadar albarkacin baki, kwarewa da walwalar ‘yan jarida gaba daya,” in ji ta.

A karshe, Kwamared Ike ta yi kira da a ci gaba da kasancewa cikin hadin kai da kwarewa a aikin jarida, tana mai jaddada kudurinta na ci gaba da daukaka kungiyar NUJ FCT zuwa matakin gaba.