Trends

Gwamnan Bauchi, Bala Mohammed, ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa APM

A wani babban sauyi na siyasa da ka iya sauya fasalin harkokin siyasa gabanin zaben 2027, Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, a ranar Asabar ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP zuwa jam’iyyar APM, tare da magoya bayansa da ke karkashin bangaren Tanimu Turaki.

Gwamnan ya bayyana matakin ne a Fadar Gwamnati da ke Bauchi, a wani taro da ya samu halartar manyan jami’an gwamnati, shugabannin jam’iyya da masu ruwa da tsaki, inda ya kasance tare da Shugaban jam’iyyar APM na kasa, Yusuf Dantalle.

Ya bayyana sauyin a matsayin “tsayayye kuma na dabarun siyasa,” yana mai cewa an yanke shawarar ne bayan tuntuba mai zurfi da abokan siyasa da masu ruwa da tsaki a fadin jihar.

“Bayan dogon tuntuba, mun dauki mataki mai tsauri da kuma na hikima na shiga jam’iyyar Allied Peoples Movement,” in ji gwamnan.

Mohammed ya kara da cewa dalilin sauyin shi ne domin sake tsara karfin siyasa gabanin zaben 2027, tare da samar da ingantaccen dandali ga magoya bayansa.

“Wannan mataki yana da manufa guda—wato samun nasara a zabukan gaba da kuma ci gaba da yi wa al’ummarmu hidima cikin gaskiya, tare da hada kan magoya baya da kuma gabatar da sahihin zabi ga jama’a,” in ji shi.

Ya kuma bayyana cewa ci gaba da kasancewa a PDP ba ya ba da tabbacin hadin kai da ake bukata domin cimma manufofin gwamnatinsa.

“A matsayinmu na shugabanni, dole ne mu samar da jagoranci mai kuzari da kuma alkibla ga mabiyanmu. Ba za mu bari jama’armu su rasa ingantaccen dandali na siyasa ba,” ya kara da cewa.

Ficewar gwamnan ta kasance babban koma baya ga PDP, musamman duba da cewa a baya ya rike mukamin Shugaban Kungiyar Gwamnonin PDP, wanda ya sanya shi cikin manyan masu fada a ji a jam’iyyar a fadin kasa.

Duk da haka, Mohammed ya nuna godiyarsa ga PDP bisa rawar da ta taka a rayuwarsa ta siyasa, yana mai cewa ita ce ta ba shi damar zama gwamna a 2019.

“Jam’iyyar PDP ta ba mu dama mu yi aiki tare da bayar da gudunmawa wajen cigaban jiharmu da kasa baki daya. Muna matukar godiya da wannan tarihi,” in ji shi.

A yayin bikin karbarsa cikin APM, Dantalle ya mika masa katin zama dan jam’iyya tare da tutar jam’iyyar da tambarinta mai dauke da rogo, a matsayin alamar karba.

“Ina maraba da kai cikin jam’iyyarmu, kuma zan fara da baka katin zama cikakken dan jam’iyya,” in ji Dantalle.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *