Matatar man fetur ta Dangote ta kara fadada tasirinta a yankin Afirka bayan ta fitar da kwale-kwalen mai guda 12 na kayayyakin mai da aka tace, wanda ya kai ton 456,000 (kimanin lita miliyan 608), zuwa kasashe biyar na Afirka.
An sayar da kayayyakin ne bisa tsarin Free on Board (FOB) ta hannun ‘yan kasuwar duniya, inda aka kai su zuwa Côte d’Ivoire, Kamaru, Tanzaniya, Ghana da Togo. Wannan na zuwa ne a matsayin wani muhimmin ci gaba bayan matatar ta kai karfin tace ganga 650,000 a rana a watan Fabrairun 2026.
Wani babban jami’in matatar ya bayyana cewa fitar da kayayyakin na nuna “karuwar amincewa da karfin Najeriya wajen tace mai da kuma sauyin tsarin samar da mai a Afirka.”
Matatar na samar da man fetur da dizal masu ingancin Euro 5, wanda hakan ya kara yawan bukata yayin da kasashen Afirka ke kokarin daina amfani da man da ba su da inganci.
Ana sa ran fitar da kayayyakin zai taimaka wajen karfafa tsaron makamashi a yankunan Yammacin Afirka, Gabashin Afirka da Tsakiyar Afirka, tare da rage dogaro da shigo da mai daga Turai da Gabas ta Tsakiya, da kuma rage kudin sufuri da jinkirin isar da kaya.
Jami’in ya jaddada cewa hakan ba zai shafi wadatar mai a cikin gida ba, yana mai cewa: “Tabbas ba zai hana biyan bukatun cikin gida ba, domin mun tsara hakan tun lokacin da muka fara gina matatar.”
Rahotanni sun nuna cewa wasu kasashen Afirka da suka hada da Afirka ta Kudu, Ghana da Kenya sun tuntubi matatar domin kulla yarjejeniyar samar da mai, sakamakon rikice-rikicen duniya da ke da alaka da yakin Iran.
Masana sun bayyana cewa wannan ci gaba zai sanya Najeriya ta zama cibiyar tace mai a yankin, tare da kara shigar kudin musayar waje da kuma sauya tsarin samar da mai a nahiyar Afirka.
