Trends

Kotu ta Umarnin Tsare Tsohon AGF Malami, Ðansa da Matarsa a Gidan Gyaran Hali na Kuje

Tsohon Antoni-Janar na Tarayya kuma Ministan Shari’a, Abubakar Malami (SAN)

Kotun Tarayya da ke Abuja, a ranar Talata, ta bayar da umarnin tsare tsohon Babban Lauyan Gwamnatin Tarayya kuma Ministan Shari’a, Abubakar Malami (SAN), a Gidan Gyaran Hali na Kuje, har zuwa lokacin da za a saurari kuma a yanke hukunci kan bukatar belinsu.

Mai shari’a Emeka Nwite, wanda ke jagorantar shari’ar, ya kuma bayar da umarnin tsare sauran wadanda ake tuhuma tare da Malami, wato ɗansa Abubakar Malami, da kuma ɗaya daga cikin matansa, Bashir Asabe.

Mai shari’a Nwite ya yanke wannan hukunci ne bayan ya saurari hujjoji daga bangaren lauyan kare kai karkashin jagorancin Joseph Daudu (SAN), da kuma lauyan masu gabatar da ƙara, Ekele Iheneacho (SAN).

Malami da sauran wadanda ake tuhumar suna fuskantar tuhume-tuhume 16 na safarar kuɗi (money laundering) da Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa (EFCC) ta shigar a kansu.

A cewar tuhumar, laifuffukan da ake zargi sun shafi shekaru da dama, kuma sun haɗa da amfani da kamfanoni da asusun banki wajen safarar kuɗi, riƙe kuɗaɗe a matsayin jinginar lamuni, da kuma sayen kadarori masu tsada a Abuja, Kano, da wasu wurare daban-daban.

Hukumar EFCC ta kuma zargi cewa wasu daga cikin laifuffukan an aikata su ne a lokacin da Malami ke rike da mukamin Babban Lauyan Gwamnatin Tarayya, lamarin da ya sabawa tanade-tanaden Dokar Hana Safarar Kuɗi ta 2011 (da aka yi wa gyara) da kuma Dokar Hana da Dakile Safarar Kuɗi ta 2022.