Kungiyar Likitocin Resident ta Ƙasa (NARD) ta umarci mambobinta da su janye ayyukansu daga asibitocin gwamnati a fadin Najeriya daga ranar Juma’a.
Matakin ya biyo bayan cikar wa’adin sa’o’i 24 da kungiyar ta bai wa Gwamnatin Tarayya domin cika bukatunsu. Wannan wa’adin ya zo ne bayan wani na kwanaki 10 da ya ƙare a ranar 10 ga Satumba ba tare da samun mafita ba.
Tun ranar 1 ga Satumba, NARD ta yi gargadin cewa za ta shiga yajin aiki na dindindin idan gwamnati ta gaza warware matsalolin cikin kwanaki 10.
Likitocin resident, wadanda su ne mafi rinjaye a cikin ma’aikatan lafiya a manyan asibitoci da na musamman, sun sha shiga yajin aiki a shekarun baya saboda albashi da ake binsu, rashin kyakkyawan yanayin aiki da walwala mara kyau.
Shugaban NARD, Dr. Tope Osundare, ya shaida wa manema labarai a ranar Alhamis cewa sabuwar wa’adi ya fito ne daga sakamakon taron kwamitin zartarwa na kasa (NEC) na kungiyar wanda aka gudanar ta yanar gizo tsawon sa’o’i shida a ranar Laraba.
Rahotanni sun nuna cewa likitocin na neman a gaggauta biyan kudaden Medical Residency Training Fund (MRTF) na shekarar 2025, biyan watanni biyar na bashin karin albashin kashi 25–35 bisa 100 na tsarin CONMESS, da sauran albashin da ake binsu tun baya.
Sauran bukatun sun hada da biyan kudaden kayan aiki (accoutrement allowance) na 2024, biyan kudaden alawus-alawus na musamman cikin lokaci, da kuma dawo da sahalewar takardun shaidar membobinsu daga hukumar horar da likitoci ta Afirka ta Yamma.
Sun kuma bukaci Kwalejin Kwararrun Likitoci ta Ƙasa ta Najeriya ta fitar da takardun shaidar membobinsu ga duk wadanda suka cancanta, aiwatar da sabon tsarin albashin 2024 (CONMESS), magance matsalolin walwalar likitocin resident a Jihar Kaduna, da kuma warware halin likitocin resident na asibitin koyarwa na LAUTECH, Ogbomoso.
Osundare ya ce kungiyar ta san da alkawarin gwamnati na warware matsalolin, amma tana bukatar a dauki mataki nan take.
Ya ce: “Gwamnatin Tarayya ta kira mu jiya kuma ta yi alkawarin warware damuwarmu. Mun gudanar da taro, bayan tattaunawa tsawon sa’o’i shida muka yanke shawarar bai wa gwamnati karin sa’o’i 24 don tabbatar da biyan MRTF ga wadanda suka cancanta, MDCN ta sabunta takardun shaidarmu da sauran bukatunmu. Idan babu wani abu da ya faru kafin ƙarshen yau (Alhamis), za mu fara yajin aiki daga gobe (Juma’a).”
Da safiyar Juma’a, Osundare ya tabbatar da fara yajin aikin ga Daily Trust.
Ya ce: “Abin takaici, mafi ƙarancin bukatunmu ba a biya su cikin wa’adin da muka bayar ba, don haka yajin aiki ya fara da safiyar yau kamar yadda NEC ta umarta.”
Da aka tambaye shi ko yajin aikin na gargadi ne, sai ya ce: “Za mu yi nazari bayan gwamnati ta yi abin da ya dace.”
Haka nan, a cikin wani sako mai taken “Sanarwar shiga yajin aiki” daga Sakatare Janar na NARD, Dr. Oluwasola Odunbaku, a ranar Juma’a, kungiyar ta tabbatar da fara yajin aikin.
Ya ce: “Barkanmu da safiya, mambobin NEC. Mun gode da hadin kai da fahimtar juna. Kamar yadda aka bayyana a sanarwar da ta gabata, yajin aiki zai fara da karfe 8:00 na safe yau (Juma’a). Dukkan shugabannin cibiyoyi su tabbatar da jagorantar mambobinsu yadda ya kamata. Za mu ci gaba da sanar da mambobin NEC bayanai daga baya.”
