Trends

Fushin Babachir da Tinubu, Rashin Zabarsa Mataimakin Shugaban Kasa – Wike

Babachir Lawan

Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike, ya ce tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya, Babachir Lawal, yana nuna fushi da shugaba Bola Ahmed Tinubu ne saboda bai zaɓe shi a matsayin mataimakin shugaban ƙasa a zaɓen 2023 ba.

Wike ya bayyana hakan ne a wata hira da aka yi da shi a tashar Channels Television, inda ya ce Lawal ya ziyarce shi a gidansa da ke Fatakwal jim kaɗan bayan Tinubu ya sanar da tsohon gwamnan Jihar Borno, Kashim Shettima, a matsayin abokin tafiyarsa.

A cewar Wike, Lawal ya nuna takaici sosai a lokacin wannan ganawa saboda ya yi tsammanin Tinubu zai zaɓe shi a matsayin mataimakin shugaban ƙasa.

“Da Shugaba Tinubu ya zaɓi Shettima, Babachir Lawal ya zo gidana a Fatakwal tare da wani tsohon Kakakin Majalisar Wakilai. Ya nuna ɓacin rai domin ya ɗauka shugaban zai zaɓe shi a matsayin mataimaki,” in ji Wike.

Wike ya yi zargin cewa sukar da Lawal ke yi wa shugaba Tinubu a ‘yan makonnin nan ba ta da nasaba da damuwa kan tafiyar da ƙasar, illa dai fushinsa na rashin samun mukamin da yake buri.

“Wani lokaci akwai mutanen da kake ɗauka da girma har sai wani lamari ya bayyana ainihin manufarsu. Fushinsa ba kan Najeriya yake ba, ba kan mulki ba ne, illa dai saboda ba a naɗa shi a matsayin mataimakin shugaban ƙasa ba,” Wike ya ƙara da cewa.

A kwanakin baya, Babachir Lawal ya bayyana Tinubu a matsayin “mai girman kai” kuma “mara kusanci,” yana gargadin cewa ƙasar na kan hanya mai haɗari a ƙarƙashin wannan gwamnati.

Sai dai Wike ya yi watsi da waɗannan kalamai, yana mai cewa maganganun Lawal ba su da gaskiya kuma babu adalci a cikinsu.

“Abin takaici ne mutum ya fito a talabijin na ƙasa yana zagin shugaban ƙasa, ba saboda matsalolin manufofi ba, amma saboda kawai bai samu mukamin da yake tsammani ba,” in ji shi.

Ministan FCT ya kuma kare tsarin mulkin shugaba Tinubu, yana mai cewa ba kowane ɗan ƙasa ne zai iya samun kai tsaye ga shugaban ƙasa ba.