Sanata Abubakar Sadiq Yar’adua, daya daga cikin masu kafa jam’iyyar All Progressives Congress (APC), ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar, yana mai zargin ta da cin amanar gwanayenta da kuma gazawa wajen kare muradun ‘yan Najeriya.
A cikin wata wasika mai dauke da kwanan wata 28 ga Yuli, wacce ya aikawa Shugaban APC na Gundumar Wakilin Gabas da ke cikin Karamar Hukumar Katsina, Sanata Yar’adua ya bayyana cewa jam’iyyar ta kauce daga manufofinta na asali, kuma ta kasa kare talakawan Najeriya.
“Ba zan ci gaba da zama cikin jam’iyyar da ta mance da ka’idojin asalinta na zama mai hidima ga al’umma ba,” in ji Yar’adua a cikin wasikar.
Yar’adua, wanda ya taka muhimmiyar rawa wajen kafa jam’iyyar Congress for Progressive Change (CPC) da daga bisani aka hade ta da wasu jam’iyyu domin kafa APC, ya bayyana cewa jam’iyyar yanzu “ta fi koma baya da rashin hangen nesa fiye da gwamnatin da ta maye gurbinta a shekarar 2015.”
Ya soki gwamnatin yanzu bisa abin da ya kira halin ko-in-kula da ta nuna ga matsalar tsaro, wahalhalun tattalin arziki da kuma take hakkin dan Adam. Ya kuma zargi shugabannin kasar da kafa manufofin tattalin arziki da suka cutar da jama’a, yana kwatanta su da “barayin birni” da suka rasa dangantaka da gaskiyar halin da talakawa ke ciki.
“Ba zan ci gaba da goyon bayan jam’iyya ko gwamnati da ba ta da kunyar kallon yadda ‘yan kasa ke fuskantar kisa, fyade, cin zarafi, tsangwama da korar su daga gidajensu ba,” in ji shi.
Sanatan ya bayyana niyyarsa ta hada kai da “masu ra’ayi daya” domin zubar da gwamnatin da ya bayyana a matsayin mugunta, son kai da cin hanci, wacce a cewarsa tana fifita muradun masu kudi da na kasashen waje akan na talakawan Najeriya.
Ya kammala wasikarsa da kira ga magoya bayansa, abokan siyasa da ‘yan uwa da su bi sahunsa zuwa jam’iyyar African Democratic Congress (ADC), wacce ya ce tana da mafi kyawun damar dawo da martabar Najeriya da aka rasa.
Ficewar Sanata Yar’adua daga APC na daukar matakin girma a siyasar Jihar Katsina, kuma na iya haifar da gagarumin canji a tsarin siyasar jihar gabanin babban zaben da ke tafe.



