Shugaban kasar Kamaru, Paul Biya, wanda ke da shekaru 92, an sanar da shi a hukumance a matsayin wanda ya ci zaben shugaban kasa na shekarar 2025.
A cewar sakamakon da Majalisar Dokokin Tsarin Mulki ta sanar, Biya ya samu kashi 53.66% na kuri’un, yayin da Issa Tchiroma ya samu kashi 35.19%.
An sanar da sakamakon ne a ranar Litinin, kodayake an gudanar da zaben a ranar 12 ga Oktoba.
Biya yanzu ya kara tsawaita mulkinsa na shekaru da dama kuma zai ci gaba da jagorantar Kamaru har na wasu shekaru 7 masu zuwa.
Cikakken bayani nan gaba…..

