Masana harkokin kiwon lafiyar jama’a da masu tsara manufofi sun bukaci Najeriya ta kara karfafa tsarin sa ido kan cututtuka domin gano sabbin barazanar lafiya da kuma mayar da martani cikin gaggawa.
An bayyana wannan bukata ne a yayin taron shekara-shekara na 12 na Kungiyar Masana Kimiyyar Yaduwar Cututtuka ta Najeriya da aka gudanar a Calabar, mai taken “Karfafa Juriyar Najeriya a Fannin Yaduwar Cututtuka: Tunkarar Sabbin Kalubalen Lafiya da Masu Dawowa.”
Shugaban kungiyar na kasa, Dakta Matthew Ashikeni, ya jaddada muhimmancin gano cututtuka da wuri tare da daukar matakan gaggawa domin dakile yaduwar su.
Ya ce, “Gano cuta da wuri da kuma mayar da martani cikin sauri na taimakawa wajen dakile barkewar cututtuka. Gina tsarin da zai iya jurewa kalubale na bukatar ingantaccen tsarin sa ido, tsaftar muhalli, ci gaba da horas da ma’aikata, da kuma manufofin lafiya da suka dogara da hujjoji.”
Ashikeni ya kuma bayyana muhimmiyar rawar da cibiyoyin bincike ke takawa wajen samar da bayanan da za su taimaka wajen tsara hanyoyin magance matsalolin lafiya. Haka kuma ya yabawa gwamnatin Jihar Cross River bisa goyon bayan da ta bayar wajen karbar bakuncin taron.
Da yake wakiltar gwamnan jihar, Bassey Otu, Kwamishinan Lafiya na jihar, Dakta Henry Ayuk, ya bayyana cewa harkokin kiwon lafiya na daga cikin manyan abubuwan da gwamnatin jihar ta ba fifiko a shirinta na ci gaba.
Ya ce gwamnatin ta zuba jari a cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko, shirye-shiryen rigakafi, inshorar lafiya da kuma kai ayyukan lafiya zuwa yankunan da ke da wahalar isa.
Ayuk ya kara da cewa jihar ta samu nasarar kai alluran rigakafi da muhimman magunguna ga al’ummomi masu rauni, yayin da tsarin inshorar lafiyar jihar ya taimaka wajen rage nauyin kudaden jinya da ke kan mazauna jihar.
Babbar Daraktar Hukumar Kula da Lafiya ta Matakin Farko ta Cross River, Dakta Vivian Otu, ta jaddada muhimmancin gina tsarin lafiya mai juriya, tana mai cewa dole ne tsarin kiwon lafiya ya kasance cikin shiri domin mayar da martani cikin sauri idan barkewar cuta ta faru.
Ta kuma yi kira da a kara hada kai da abokan hulda na ci gaba domin gina tsarin lafiya da zai fi saurin amsa bukatun jama’a.
A nata bangaren, wakiliyar World Health Organization, Dakta Rebecca Olatunde, ta bukaci masana su ci gaba da wayar da kai kan muhimmancin sa ido kan cututtuka, tana mai gargadin cewa wajibi ne a dauki matakan gaggawa wajen tunkarar barazanar lafiyar jama’a domin kare al’umma.
