Trends

Kotun ta ba Nasir El-Rufai Belin N200m, Ta Hana Shi Yin Hira da Yan Jarida

Mallam Nasir El-Rufai Tsohon gwamnan Kaduna

Kotun Tarayya da ke zamanta a Kaduna ta bayar da belin Naira miliyan 200 ga tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, kan zarge-zargen cin hanci da rashawa da Independent Corrupt Practices and Other Related Offences Commission (ICPC) ta shigar a kansa.
Sai dai kotun ta umarci cewa dole ne tsohon gwamnan ya ci gaba da zama a hannun hukumar ICPC har sai ya cika dukkan sharuddan belin.

Alkalin shari’ar, Mai Shari’a Rilwanu Aikawa, ne ya yanke hukuncin bayan dage sauraron karar daga ranar 1 ga Afrilu zuwa 14 ga Afrilu, 2026 domin nazarin hujjojin bangarorin da ke karar.

Kotun ta amince da belin ne da sharadin biyan Naira miliyan 200 tare da mutane biyu da za su tsaya masa, inda alkalin ya bayyana sharuddan a matsayin “masu tsauri da yawa.”

A cewar kotun, dole ne wanda ake kara ya ci gaba da zama a hannun ICPC har sai an cika dukkan sharuddan belin.
Daga cikin sharuddan, mutanen da za su tsaya masa dole su ajiye fasfo dinsu a gaban kotu.

Haka kuma, daya daga cikin masu tsaya masa dole ne ya kasance ma’aikacin gwamnati ba kasa da mataki na 15 ba, yayin da dayan kuma dole ne ya kasance sarki ko wani babban mai sarauta da aka amince da shi.
Bugu da kari, an hana El-Rufai yin duk wani bayani ga jama’a dangane da shari’ar, kuma dole ne ya rika halartar duk zaman kotu.

Martani
Lauyan tsohon gwamnan, Ubong Akpan, ya ki yin tsokaci ga manema labarai bayan kammala zaman kotun.
Sai dai dan El-Rufai, Bello El-Rufai, ya tabbatar da cewa an ba mahaifinsa beli.

Haka zalika, wani jigo a jam’iyyar African Democratic Congress (ADC), Hayatudeen Makarfi, ya tabbatar da lamarin, yana mai cewa belin ya zo da sharudda da dama, ciki har da kudi, kadarorin fili, da kuma tsayawar wani sarki a matsayin wanda zai lamunce masa.

Ya kara da cewa dole ne a cika wadannan sharudda kafin tsohon gwamnan ya samu ‘yanci, yana mai jaddada cewa zai ci gaba da zama a hannun ICPC har sai an bi ƙa’idojin.

Wata Shari’a Dabam
Tun da fari a ranar Talata, wani zama a Babbar Kotun Jihar Kaduna kan wata shari’a mai alaka da wannan ya tsaya cak, bayan da kotun ta dage yanke hukunci kan bukatar belin El-Rufai zuwa ranar 21 ga Afrilu, 2026.

An dage zaman ne sakamakon rashin damar alkalin da ke jagorantar shari’ar, Mai Shari’a Darius Khobo, na fitar da hukunci kamar yadda aka tsara.
A ranar 18 ga Maris, 2026, ICPC ta gurfanar da El-Rufai tare da daraktan kamfanin TMDK Terminal Limited, Amadu Sule, a gaban Babbar Kotun Jihar Kaduna karkashin shari’a mai lamba KDH/KAD/ICPC/01/26.
Zarge-zargen sun hada da amfani da mukami ba daidai ba, zamba, yunkurin aikata zamba, da kuma bai wa wasu gata ba bisa ka’ida ba.
Sai dai daga baya masu gabatar da kara sun gyara tuhume-tuhumen, inda suka cire sunan Sule daga cikin shari’ar, tare da takaita karar ga El-Rufai kadai.
Da yake magana bayan dage zaman kotun, Akpan ya danganta lamarin da wasu dalilai da ba su karkashin ikon kotun ba.
“Mai shari’a yana cikin jimami ne, don haka bai samu damar kammala hukuncin ba. Muna fahimtar irin wadannan abubuwa na faruwa,” in ji shi.
Ya kuma bayyana fatan alheri gabanin sabon ranar yanke hukunci, yana mai cewa za a saurari batun belin a mako mai zuwa.
Sai dai Akpan ya zargi ICPC da gudanar da shari’o’i a matakai daban-daban kan abokin aikinsa, yana mai cewa ana ci gaba da shari’o’i a kotunan jiha da ta tarayya a lokaci guda.

Bayan zaman Babbar Kotun Jihar Kaduna, an wuce da El-Rufai zuwa Kotun Tarayya, inda aka sake gurfanar da shi kan wasu tuhume-tuhume guda 10 a gaban Mai Shari’a Aikawa.
Lamarin na nuni da yadda tsohon gwamnan ke fuskantar kalubalen shari’a a kotuna daban-daban a lokaci guda.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *