Gwamnatin Tarayya ta Najeriya ta kaddamar da wani asusun lamuni na dala biliyan 1 mai suna AfCFTA Adjustment Fund Credit Facility, domin taimaka wa ‘yan kasuwa su faɗaɗa samarwa, sabunta harkokinsu, da ƙara fitar da kayayyaki a ƙarƙashin yarjejeniyar cinikayya ta nahiyar Afirka (AfCFTA).
Ministar Masana’antu, Kasuwanci da Zuba Jari, Jumoke Oduwole, ta sanar da wannan shiri a taron Kwamitin Gudanar da AfCFTA da aka gudanar a Abuja, inda ta bayyana shi a matsayin wata muhimmiyar dama ta ƙarfafa gasa da Najeriya ke yi a kasuwar nahiyar Afirka.
Ta ce duk da ci gaban da Najeriya ta samu wajen aiwatar da AfCFTA, har yanzu ‘yan kasuwa da dama na fuskantar ƙalubale kamar cika takardu, samun takardar shaida, bin ƙa’idojin inganci, da kuma samun damar shiga kasuwanni.
Gwamnati na ƙoƙarin magance waɗannan matsaloli ta hanyar sauƙaƙe jagororin kasuwanci, inganta hanyoyin sauƙaƙe cinikayya, da haɗin gwiwa da Hukumar Kwastam da Hukumar Bunƙasa Fitar da Kaya.
Oduwole ta kuma jaddada muhimmancin daidaita dokokin AfCFTA a cikin gida, musamman yarjejeniyar kasuwancin dijital (Digital Trade Protocol), domin sanya Najeriya a sahun gaba a sabuwar tattalin arzikin dijital na Afirka.
Mai kula da AfCFTA a matakin ƙasa, Patience Okala, ta bayyana cewa shirye-shiryen wayar da kai da aka gudanar a Kano sun jawo hankalin ‘yan kasuwa 470, ciki har da mata ‘yan kasuwa da dama.
Ta ce sabon shirin AfCFTA ABC Series na ba kamfanoni ilimin yadda ake fitar da kaya zuwa kasashen waje cikin sauƙi da aiki na gaskiya.
Okala ta bayyana cewa wannan asusu na dala biliyan 1 an tsara shi ne domin manyan kamfanonin Afirka da ke da ikon samun lamuni na aƙalla dala miliyan 10, kuma Najeriya na shirin zaɓar rukunin kamfanoni na gwaji domin cin gajiyar shirin.
Wani mataimakin darakta a Hukumar Bunƙasa Fitar da Kaya ta Najeriya (NEPC), Mista Njoku, ya ce dole masu fitar da kaya su yi rajista da hukumar domin samun tallafi kamar Export Expansion Grant.
Ya tabbatar da cewa an mayar da tsarin rajistar cikakken na dijital, kuma takardar shaida tana aiki na tsawon shekaru biyu.
Masu ruwa da tsaki a taron sun jaddada aniyar ƙara buɗe dama ga mata da matasa ‘yan kasuwa, ƙarfafa haɗin gwiwar hukumomi, da faɗaɗa rawar Najeriya a sarkar samar da kaya ta yanki, tare da burin rage dogaro da mai da kuma ƙara faɗaɗa fitar da kayayyaki zuwa kasashen waje.
