Majalisar Wakilai ta amince da karɓar rancen waje na dala miliyan $516 da Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya nema domin tallafa wa wasu sassan aikin titin Sokoto–Badagry Superhighway.
An bayar da amincewar ne yayin zaman majalisa a Abuja, bayan mataimakin shugaban kwamitin majalisar kan tallafi, rance da kula da bashi, Abdullahi Rasheed ya gabatar da rahoton kwamitin.
Tun da farko, Tinubu ya rubuta wa Majalisar Dokoki ta Ƙasa yana neman amincewa da rancen dala $516,333,007 daga Deutsche Bank AG, wanda ke da goyon bayan wani ɓangare na garanti daga Islamic Corporation for the Insurance of Investment and Export Credit.
Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio ya kare shirin karɓar bashin, yana mai cewa: “Ya fi kyau a ci bashi domin ayyuka da gine-ginen ƙasa, domin daga ƙarshe za a iya biya ta hanyar amfanin da aka samu daga waɗannan ayyuka.”
Za a yi amfani da rancen ne wajen aiwatar da sassa na 1, 1A da 1B na aikin, wanda ya kai kusan kilomita 120 a matakin farko. Gaba ɗaya aikin zai kai kilomita 1,000, yana haɗa jihohin Sokoto, Kebbi, Neja, Kwara, Oyo, Ogun da Legas, daga Illela zuwa Badagry.
Rancen na da wa’adin shekaru tara, ciki har da shekaru uku na sassauci kafin fara biya, tare da ribar da aka ɗaura kan tsarin SOFR + kashi 5.3% a shekara.
Haka kuma, Gwamnatin Tarayya za ta bayar da naira biliyan ₦265 a matsayin nata gudummawar domin biyan kuɗin sayen fili da sauran buƙatu.
Duk da goyon bayan ‘yan majalisa ga aikin, wasu masu sukar matakin sun nuna damuwa kan yadda bashin ƙasar ke ƙaruwa. Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar ya tambayi yadda ake tafiyar da harkokin kuɗi, yayin da masani Seun Onigbinde ya yi gargadi kan bashin da ba a tsara yadda ya kamata ba.
Bayanan Debt Management Office sun nuna cewa kuɗin biyan basussuka ya kai naira tiriliyan ₦16 a shekarar 2025, wanda ya ƙaru da kashi 22.9% idan aka kwatanta da 2024. Haka kuma, basussukan waje sun kai kusan rabin wannan adadi, abin da ke nuna matsin lamba da ke ƙaruwa a kan tattalin arzikin Najeriya.







