Tattaunawar Annoba: Najeriya Za Ta Karbi Bakuncin Kasar Sin

Gwamnatin Tarayya za ta karbi bakuncin wani muhimmin taro na tattaunawa kan tsaron lafiya da shirye-shiryen tunkarar annoba a Abuja ranar 30 ga Maris, 2026.

Taron, mai taken “Lessons on Pandemic Preparedness and Response: Insights from China and Nigeria”, zai hada manyan jami’an gwamnati, cibiyoyin kiwon lafiya na duniya, masu tsara manufofi, da masana kimiyya daga Najeriya da kasar Sin.

Ma’aikatar Lafiya da Jin Dadin Jama’a ta bayyana cewa manufar taron ita ce karfafa tsarin sa ido kan cututtuka, hanyoyin gargadi da wuri, hadin kai wajen daukar matakan gaggawa, da kuma juriya na tsarin kiwon lafiya.

Ministan Lafiya mai kula da harkokin tsari, Muhammad Ali Pate, ya ce wannan taro yana nuna kudurin Najeriya na gina tsarin kiwon lafiya mai karfi bayan darussan da aka koya daga annobar COVID-19.

Za a kuma tattauna kan muhimmancin amincewar al’umma, isar da sahihan bayanai game da hadari, da hadin gwiwar kasa da kasa. Haka kuma, za a duba hanyoyin zurfafa hadin gwiwar Najeriya da kasar Sin a bangaren binciken kiwon lafiya, dakunan gwaje-gwaje, sa ido kan kwayoyin cuta, da musayar fasaha.

Ana sa ran sakamakon taron zai hada da samar da shawarwari kan manufofi, kara dankon zumunci tsakanin kasashen biyu, da kuma dabarun da za su taimaka wajen tsara manufofin tsaron lafiya na kasa.

Shirin zai kunshi jawaban bude taro daga jami’an gwamnati, babban jawabi daga kwararren masani a fannin kiwon lafiya na duniya, tattaunawar bangarori daban-daban, da kuma taron manema labarai bayan kammala taron.

Jami’ai sun ce wannan tattaunawa za ta samar da darussa masu amfani tare da karfafa hadin gwiwa domin tabbatar da cewa Najeriya ta fi shiri wajen fuskantar barazanar cututtuka a nan gaba.