Trends

Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Tabbatar da Dakatar da Sanata Natasha

Sashen Kotun Ɗaukaka Ƙara da ke Abuja, a ranar Litinin, ya tabbatar da matakin da Majalisar Dattawa ta ɗauka na dakatar da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, inda ta ce majalisar ta yi aiki ne a cikin ikon da doka ta ba ta.

A hukunci guda ɗaya da kwamitin alƙalai uku ya yanke a ƙarar da Natasha ta shigar kan Magatakardar Majalisar Ƙasa da wasu mutane uku, mai lamba CA/ABJ/CV/1107/2025, kotun ta yanke cewa dakatarwar ba ta tauye haƙƙin majalisa ko na kundin tsarin mulkin Sanata Akpoti-Uduaghan ba.

Sai dai kotun ta soke shari’ar raini da kuma tarar Naira miliyan biyar (₦5m) da aka kakaba mata kan wata wasikar neman afuwa ta barkwanci da ta yi wa Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio.

Da yake karanta babban hukuncin, Mai Shari’a Abba Muhammed ya ce Shugaban Majalisar Dattawa ya bi ƙa’idojin majalisa ne wajen hana Akpoti-Uduaghan yin magana a zaman majalisa na ranar 20 ga Fabrairu, 2025, domin ba ta zauna a kujerar da aka ware mata a hukumance ba.

Kotun ta bayyana cewa dokokin Majalisar Dattawa sun bai wa Shugaban Majalisa ikon sake ware kujeru ga sanatoci, kuma ana yarda sanatoci su yi magana ne kawai daga kujerun da aka ware musu.

Kotun Ɗaukaka Ƙara ta ce Sanata Natasha ta yi kuskure a abin da ya faru ranar 20 ga Fabrairu, 2025, lokacin da Shugaban Majalisa ya sake ware mata sabuwar kujera amma ta ƙi bin umarnin.

Haka kuma kotun ta ce ikirarin Natasha na cewa ba a ba ta sanarwa tun da wuri kan sauyin kujera ba shi da tushe, domin babu wani tanadi a dokokin majalisa da ke buƙatar irin wannan sanarwa.

A hukuncin da alƙalan suka yanke baki ɗaya, Mai Shari’a Muhammed ya ce Kotun Tarayya ta Ƙasa (Federal High Court) tun da farko ya kamata ta ƙi karɓar shari’ar, bayan da ta gano cewa Majalisar Dattawa ta yi aiki ne bisa tanadin da ke ba ta damar dakatar da duk wani mamba da ya yi kuskure.

Kotun Ɗaukaka Ƙara ta ce Sanata Natasha, bayan an sanar da ita sauyin kujera, ya dace ta koma sabuwar kujerar, tana mai ƙara da cewa Majalisar Dattawa ta yi daidai da aiwatar da doka ta shida (Order Six) sakamakon ci gaba da ƙin bin umarnin majalisa da ta yi.

Kotun ta kuma ce ƙin amsa gayyatar Kwamitin Majalisar Dattawa kan Ɗa’a, Ƙorafe-ƙorafe da Ƙuntatawa (Ethics, Petitions and Privileges) da Sanata Natasha ta yi bai taimaka mata ba.

Haka zalika, Kotun Ɗaukaka Ƙara ta yi watsi da ƙarar da Natasha ta shigar cewa an dakatar da ita ne bisa saɓa wa umarnin Mai Shari’a Obiora Egwuatu, inda ta ce tun da Mai Shari’a Egwuatu ya janye kansa daga shari’ar kuma Mai Shari’a Binta Nyako ta fara shari’ar daga farko, umarnin Egwuatu bai ƙara aiki ba.
Sai dai kotun ta yi kuskure ga tuhumar raini da kuma tarar Naira miliyan biyar da Mai Shari’a Binta Nyako ta kakaba wa Sanata Natasha.

A cewar Kotun Ɗaukaka Ƙara, gazawar kotun ƙasa wajen miƙa takardun shari’a Forms 48 da 49 ga Sanatar Kogi ya lalata shari’ar raini gaba ɗaya.
Saboda haka, kotun ta soke shari’ar raini da kuma tarar Naira miliyan biyar da aka kakaba wa Sanatar Kogi.