Gwamnatin jihar Anambra ta haramta wa ɗalibai yin rubutun aikin gida a cikin littattafan makaranta, tana bayyana wannan dabi’a a matsayin asara kuma ba mai dorewa ba.
Kwamishinan Ilimi na jihar, Farfa Ngozi Chuma-Udeh, ce ta bayar da wannan umarni ga makarantu a ranar Juma’a a Awka, yayin wani taron bita da aka shirya wa masu makarantu masu zaman kansu da malamai.
Farfa Chuma-Udeh ta bayyana cewa an yanke wannan hukunci ne domin a tabbatar da cewa littattafan za su iya sake amfani da su, musamman ’yan’uwan ɗalibai ƙanana da za su buƙaci littattafan idan sun shiga aji na gaba.
Ta kuma jaddada muhimmancin littattafan da ke ɗauke da abubuwan da suka haɗa kowa, suna nuna bambance-bambance, da tallafa daidaito tare da biyan bukatun dukkan ɗalibai.
“Gwamnati ba za ta lamunci karya wannan umarni ba. Ina kira ga iyaye, malamai da shugabannin makarantu su tabbatar da bin wannan doka yadda ya kamata.
Masu ruwa da tsaki su rika kai rahoton duk wani kaso na saba wa wannan umarni zuwa Ma’aikatar Ilimi,” in ji ta.
Kwamishinar ta kara da cewa wannan shiri na daga cikin dabarun gwamnatin Gwamna Charles Soludo na rage nauyin kuɗi da ke kan iyalai tare da inganta ilimi mai inganci da dorewa.
