Hon. Emberga ya Gaji Dajoh a Matsayin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Benue

Hon. Berger Alfred Emberga Sabon Kakakin Majalisar Jihar Benue

Hon. Berger Alfred Emberga ne aka zaɓa sabon Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Benue.

Zabensa ya biyo bayan murabus ɗin da tsohon kakakin, Hon. Hyacinth Dajoh, ya yi ta hanyar miƙa wasiƙar da ya rubuta da hannunsa ga Magatakardar majalisar a ranar 24 ga Agusta, 2025.

A zaman gaggawa da aka gudanar ranar Lahadi, 25 ga Agusta, ‘yan majalisar suka zaɓi Emberga domin jagorantar majalisar ta 10, a matsayin wanda zai cike gurbin shugabanci da murabus ɗin Dajoh ya haifar.

A cikin wasiƙar murabus ɗinsa, wacce ta bazu cikin sauri a shafukan sada zumunta, Dajoh ya gode wa abokan aikinsa bisa damar da suka bashi ya kasance “na farko cikin daidaito.” Ya kuma tabbatar da cewa zai ci gaba da gudanar da ayyukansa a matsayin wakilin mazabar Gboko West State Constituency.