Wani jigon jam’iyyar All Progressives Congress (APC), Edward Okocha, ya bayyana cewa Sanata Orji Uzor Kalu na da cikakken shiri da matsayin da zai tsaya takarar shugabancin majalisar dattawa a shekarar 2027, tare da yin kira ga tsohon mataimakin gwamnan Jihar Abia, Ude Oko Chukwu, da ya janye burinsa na neman kujerar sanata.
Chukwu, wanda ya rike mukamin mataimakin gwamna daga shekarar 2015 zuwa 2023, kwanan nan ya fice daga jam’iyyar PDP zuwa Labour Party (LP) tare da magoya bayansa. Wannan mataki ya haifar da rade-radin cewa yana da niyyar yin takara don kujerar majalisar dattawa ta Abia North.
A cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi, Okocha ya gargadi Chukwu da kada ya kalubalanci Kalu, wanda ke wakiltar Abia North a halin yanzu, yana bayyana shi a matsayin “ƙarfi mai ƙarfi” da kuma “babban ɗan takara” ga shugabancin majalisar dattawa.
“Mai girma Sanata Orji Uzor Kalu ya kasance yana yin aiki tukuru a majalisar dattawa, inda yake kawo muhimman ayyuka da shirye-shiryen tallafawa al’umma a yankinmu,” in ji Okocha.
Ya jaddada cewa “kwarewar Kalu a harkokin majalisa da matsayinsa na dattijo” ya riga ya ba Abia North matsayi na musamman a majalisar tarayya, inda burinsa na neman shugabancin majalisar dattawa zai iya bude manyan damar ci gaba ga yankin.
“Yayin da muke kallon shekara ta 2027, Abia North za ta fi amfana idan ta hade kai wajen sake zabin Sanata Orji Uzor Kalu, domin hakan zai kara masa damar rike manyan mukamai a majalisar dattawa,” in ji shi.
Okocha ya kara da cewa jagorancin Kalu zai kasance “sabon salo mai sauya al’amura” ga mutanen Abia North, tare da kira ga shugabanni da su hada karfi wuri guda domin marawa shi baya.







