Zaben 2027: Atiku Zai Kara Fuskantar Kaye, Tambuwal “Kaho Marar Nama” – Wike
Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike, yayi kalamai mai zafi kan tsohon Gwamnan Jihar Sakkwato, Aminu Tambuwal, inda ya bayyana shi a matsayin “kaho marar nama”, yana mai karyata tasirin sa a siyasar Najeriya musamman yayin da ake shirye-shiryen zaben 2027. Da yake magana a wata hira da aka yi da shi a shirin…
